in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun gwamnatin Somaliya sun hallaka masu dauke da makamai 30 na Al-Shabab
2019-02-11 11:38:59 cri
Bisa labarin da aka samu daga Mogadishu, babban birnin kasar Somaliya, hukumar sojan kasar ta sanar a ranar 9 ga wata cewa, bisa taimakon ofishin kwamandan sojojin Amurka dake Afirka, dakarun gwamnatin Somaliya sun dauki matakan dakile kungiyar Al-Shabab a jihar Lower Jubba dake kudancin kasar, inda aka hallaka masu dauke da makamai 30 na kungiyar.

A wannan rana da safe kuma, ofishin kwamandan sojojin Amurka dake Afirka ya sanar da cewa, a ranar 8 ga wata, sojojin Amurka sun dauki matakin kai hari ta sama ga sansanin kungiyar Al-Shabab dake kusa da garin Kismayo, inda ake da tashar teku dake kudancin kasar Somaliya, amma bai sanar da adadin mutanen da suka mutu ko suka ji rauni a sakamakon wannan harin ta sama ba.

Kungiyar Al-Shabab, wata kungiyar masu tsattsaurar ra'ayi ce dake da alaka da kungiyar Al-Qaeda. A 'yan shekarun baya bayan nan, ta sha kai hare-haren ta'addanci a kasar Somaliya ko sauran kasashe wadanda suke makwabtaka da kasar ta Somaliya. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China