Li Zhanshu ya nuna yabo ga kasar Burkina Faso domin ta sake kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninta da kasar Sin da kuma goyon bayan da take nunawa ga ka'idar Sin daya tak.
A nasa bangare, Sakandé ya bayyana cewa, kasarsa za ta ci gaba da sa kaimi ga raya dangantakar sada zumunta a tsakaninta da Sin bisa tushen ka'idar Sin daya tak, da kara yin hadin gwiwa da juna don amfanawa jama'ar kasashen biyu. (Zainab)