in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yabawa kudurin Burkina Faso na yanke huldar diflomasiyya da Taiwan
2018-05-25 18:55:01 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lu Kang ya ce kasarsa ta yaba da sanarwar da gwamnatin Burkina Faso ta bayar ta yanke huldar diflomasiyya da yankin Taiwan.

Lu ya bayyana haka ne a yayin taron manema labaru da aka shirya a yau Juma'a, inda ya ce, kudurin ya dace da muradun jama'ar Burkina Faso, kuma ya nuna cewa, kasashen duniya na martaba manufar kasar Sin daya tak a duniya. Baya ga haka, Lu ya ce, kasar Sin na son gudanar da hadin kai irin na samun moriyar juna bisa tushen girmama juna da zaman daidaiwa daida tare da duk kasashen dake zumunta da ita.(Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China