in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin, Amurka da EU za su taimakawa 'yan Zimbabwe da suka makale sakamakon mahaukaciyar guguwar Idai
2019-03-20 20:54:52 cri
Rahotanni na cewa, karin kungiyoyi na kawo dauki don taimakawa wadanda mahaukaciyar guguwar nan mai tafe da ruwan sama ta Idai da ta yi barna a kasaer Zimbabwe tsakanin ranakun Jumma'a da Lahadi.

Jakadan kasar Sin a Zimbabwe Guo Shaochun ya bayyana a yayin mika kayayyakin da ya gudana ranar Laraba da safe cewa, za a aika kayayyakin zuwa yankunan da bala'in ya fi tsanani dake lardin Manicaland.

Shi ma ofishin jakadancin Amurka ya sanar a jiya Talata cewa, zai raba dala 100,000 ta hukumar raya kasashe na Amurka. Yayin da kungiyar tarayyar Turai a nata bangaren ta sanar a jiya cewa, ta baiwa Mozambique taimakon gaggawa na Euro miliyan 2, sai Euro miliyan 1 ga kasar Malawi yayin da Zimbabwe kuma ta samu Euro miliyan 0.5.

A nata bangaren kasar Tanzaniya, ta aike da maganguna a ranar Talata, yayin da wasu karin magungunan daga hadaddiyar daular Larabawa za su iso kasar a yau Laraba.

Wasu daga cikin kasashen Afirka da suka yi alkawarin taimakawa, sun hada da Afirka ta kudu, Namibia da Angola. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China