An dai bude taron ne a yau Litinin, inda ake sa ran tattauna batutuwa da suka jibanci cinikayya, da zuba jari tsakanin kasashen Afirka, da batun samar da karin kariya ga manufofin nahiyar da masana'antun ta, da ingiza ci gaban sassa masu zaman kan su ta fannin samar da ababen more rayuwa da zirga zirga, da tsara tarukan karawa juna sani, da bincike game da hadin gwiwar kamfanonin hukuma da masu zaman kan su.(Saminu Alhassan)