in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Amurka sun hallaka mayakan al-Shabab 13 a kudancin Somalia
2019-02-03 15:45:40 cri
Rundunar sojojin Amurka dake yankunan Afirka ta AFRICOM ta ce ta hallaka dakarun kungiyar Al-Shabab 13, sakamakon hari ta sama da ta kaddamar kan mayakan a Gandarshe dake jihar Lower Shebelle na kasar Somalia.

Rundunar wadda ta bayyana hakan a jiya Asabar cikin wata sanarwa, ta ce ta kaddamar da harin ne a ranar Juma'a, kuma babu wani farar hula da ya rasu, ko ya jikkata sakamakon harin.

AFRICOM ta kara da cewa, a baya mayakan Al-Shabab din sun yi amfani da yankin Gandarshe, mai nisan kilomita 48 daga kudu maso yammacin birnin Mogadishu, fadar mulkin kasar, domin kaddamar da hare-hare da ababen fashewa, ta amfani da ababen hawa kan mazauna babban birnin kasar.

A ranar 15 da 16 ga watan Disambar da ya shude ma, sojojin Amurkan sun kaddamar da hare-hare ta sama guda shida, wadanda suka hallaka mayakan mungiyar 62, a wani wuri dake kusa da Gandarshe, wurin da a cewar tawagar ta AFRICOM, Al-Shabab ta shirya amfani da shi wajen kaiwa sansanin sojojin gwamnatin Somalia dake wurin hari.

Har ila yau a Larabar da ta gabata ma, wani harin ta sama da sojojin suka kaddamar, ya yi sanadin hallaka mayakan kungiyar 24 a yankin Hiran mai makwaftaka da Gandarshe. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China