in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Amurka za su gudanar da sabbin zagayen tattaunawa kan cinikayya a Beijing da Washington
2019-03-21 19:29:37 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin cinikayya ta kasar Sin Gao Feng, ya shaidawa taron manema labarai da ya gudana a nan birnin Beijing cewa, manyan jami'an Sin da Amurka za su gudanar da zagaye na 8 na tattaunawa kan tattalin arziki da cinikayya daga ranakun 28 zuwa 29 ga wata a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin

Jami'in ya ce, an gayyaci wakilin Amurka a fannin cinikayya Robert Lighthizer da sakataren baitul-malin Amurka Steven Mnuchin zuwa kasar Sin don wannan tattaunawa.

A bangare daya kuma, shi ma mataimakin firaministan kasar Sin Liu He, mamban hukumar siyasa na kwamitin koli na JKS kana jagoran bangaren kasar Sin a tattaunawar cinikayya da tattalin arziki tsakanin Sin da Amurka an gayyace shi zuwa Washington D.C. don halartar zagaye na 9 na tattaunawar sassan biyu da aka shirya yi a farkon watan Afrilun wannan shekara.

A baya-bayan nan, sassan biyu sun sha yin tattaunawa ta wayar tarho kan batutuwan da suka shafi tattalin arziki da cinikayya, inda suka amince su gudanar da zagaye na 8 da na 9 na tattaunawa tsakanin manyan jami'an kasashen biyu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China