in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya rubuta wasika ga makarantar "Vittorio Emanuele II" ta Rome don ba da amsa
2019-03-18 16:13:08 cri
Gabannin ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai kasar Italiya, shugaban makarantar "Vittorio Emanuele II" ta Rome, da daliban dake makarantar su 8 sun rubuta wasika zuwa ga shugaba Xi, don nuna maraba da ziyarar, da fatan su na gudanar da aikin sada zumunci a tsakanin kasashen Sin da Italiya. Shugaba Xi Jinping kuma a nasa bangaren ya rubuta musu wasika don ba da amsa, inda ya ba su kwarin gwiwar ba da gudummawar cudanyar al'adu a tsakanin kasashen biyu.

Baya ga haka, a cikin wasikar Xi Jinping ya ce, makarantarsu ta cimma nasarar kafa makarantar sakandare ta kasa da kasa ta Sinanci dake karatu a fannonin da suka shafi ilmin lissafi da sauransu, kuma ta horar da matasa masu nufin gudanar da aikin sada zumunta tsakanin Sin da Italiya masu yawa. Xi Jinping ya kuma yaba sosai da makarantar, sakamakon kokarinta na inganta musayar ra'ayoyi da cudanyar al'adu a tsakanin matasan kasashen biyu, da ciyar da zumunta a tsakanin jama'ar kasashen biyu gaba. A cewarsa, yana maraba da daliban makarantar su yi karatu da aiki a kasar Sin, yana mai fatan kasar Sin za ta kasance wurin da za su cimma burinsu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China