Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sakon jaje ga gwamna janar na New Zealand Patsy Reddy, bisa mummunan harin da aka kai birnin Christchurch na kasar a jiya Juma' a.
Cikin sakonsa, shugaba Xi ya ce, ya kadu da jin labarin harbe-harben da suka rutsa da mutane da dama.
Ya ce, a madadin gwamnati da al'ummar kasar Sin da ma shi kansa, yana jajantawa tare da mika ta'aziyya ga gwamnati da al'ummar New Zealand, yana kuma mai yi wa wadanda suka raunana fatan samun sauki cikin gaggawa. (Fa'iza Mustapha)