in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sudan ya yi fatan inganta huldar kasarsa da Rasha
2019-03-17 16:14:13 cri
Jiya Asabar 16 ga wata, shugaba Omar al-Bashir na kasar Sudan ya bayyana fatansa na inganta huldar dake tsakanin kasarsa da kuma kasar Rasha.

Shugaban Sudan ya bayyana haka ne yayin da yake ganawa da Mikhail Bogdanov, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Rasha kuma wakilin musamman kan batun yankin Gabas ta Tsakiya a wannan rana a birnin Khartoum, babban birnin kasar.

Bisa sanarwar da fadar shugaban kasar Sudan ta bayar, an ce, a yayin ganawar, shugaba al-Bashir ya ce, inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashen 2 a fannonin siyasa, tattalin arziki da cinikayya ya dace da moriyarsu duka.

Mikhail Bogdanov ya yiwa kafofin yada labaru bayani bayan ganawar cewa, bangarorin 2 sun tattauna hadin gwiwar dake tsakanin Rasha da Sudan ta fuskar tattalin arziki da cinikayya, da kuma baiwa jami'an Sudan horo da makamantansu. Haka kuma, kasar Rasha za ta karfafa huldar dake tsakaninta da Sudan ta fuskar siyasa, tattalin arziki da ciniki, ta kuma yaba da matsayin da Sudan ke tsayawa a kai na sanin ya kamata kuma cikin daidaito kan batutuwan kasa da kasa, da batun Afirka da na yankin Gabas ta Tsakiya. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China