in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Abu ne da ya zama wajibi ga gwamnatin Xinjiang ta dauki matakan yaki da tsattsauran ra'ayi in ji wani jami'i
2019-03-14 20:14:26 cri
Tawagar wakilan gwamnatin kasar Sin dake halartar taron MDD game da kare hakkin bil Adama, sun gabatarwa mahalarta taro daga kasashen daban daban, irin ci gaba da Sin ta samu wajen ciyar da yankin Xinjiang na Uygur mai cin gashin kansa gaba.

Yu Jianhua, shi ne jagoran tawagar ta Sin, a taron na MDD dake gudana a birnin Geneva. Yayin wani taro da ya gudana a gefen babban taron, ya bayyana cewa, yankin Xinjiang a yanzu, na samun ci gaba cikin sauri, da daidaito sama da wanda ya taba samu a baya. Kaza lika daukacin kabilun yankin na samun kariyar da ta dace ta fuskar tattalin arziki, da siyasa, da zamantakewar al'umma, da raya al'adu, da kuma kare hakkin muhalli.

Sai dai a cewar Yu Jianhua, saboda dalilai na siyasa, wasu na yada jita jita, da karairayi, game da abun da ke faruwa a yankin na Xinjiang, da nufin bata sunan Sin da gwamnatin ta. Sai dai kuma jami'in ya ce ko shakka babu, masu wannan ra'ayi ba za su yi nasara ba, duba da irin nasarori, da ci gaba, da daidaito, da hadin kai da ake samu a yankin na Xinjiang.

Jami'in ya kara da cewa, samar da ilimin sana'o'i, da cibiyar horaswa dake Xinjiang sun dace da bukatar yankin. Har ila yau kasar Sin ba za ta taba barin 'yan ta'adda, da masu tsattsauran ra'ayin addini, su tarwatsa abubuwa muhimmai da al'ummar yankin Xinjiang suka gina domin samar da ingantacciyar rayuwa ba.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China