Tawagar kasar Sin dake halartar wani taron MDD ta gabatar wa ma'aikatan diflomasiya da wakilai irin nasarorin da aka samu a fannin kare hakkin bil-Adam a jihar Xinjiang ta Uygur mai cin gashin kanta ta kasar Sin.
A kwanakin nan ne, wasu jami'an diflomasiya suka ziyarci jihar ta Xinjiang. Kuma sun nuna wa mahalarta taron abin da suka ji suka kuma gani a jihar, duk sun bayyana tabbaci game da makoma da ma zaman lafiyar jihar. (Ibrahim Yaya)