Shugabannin tawagogin Sin da Amurka masu tattauna batun tattalin arziki sun zanta ta wayar tarho
A yau Talata, mamban kwamitin siyasa na kwamitin tsakiyar jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kana mataimakin firaministan kasar, wanda ke jagorantar tawagar kasar Sin a shawarwarin da ake yi tsakanin Sin da Amurka kan batun tattalin arziki, Liu He, ya tattauna ta wayar tarho da wakilin kasar Amurka mai kula da batun kasuwanci Robert Lighthizer, da ministan kudin kasar Steven Mnuchin, inda bangarorin 2 suka yi musayar ra'ayi kan yadda za a tabbatar da wani rubutaccen bayanin da za a fitar bayan shawarwarin, kana an tanadi ayyukan da za a yi nan gaba. (Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku