A ranar Lahadin da ta gabata ne, jirgin kamfanin Ethiopian Airlines ya tashi daga Addis Ababa dake Habasha da niyyar zuwa Nairobi na kasar Kenya. Sai dai jirgin ya fadi mintuna kadan bayan tashinsa, lamarin da ya yi sanadin mutuwar dukkan fasinjoji da ma'aikata 157 dake ciki baki daya, ciki har da wasu Sinawa 8.
Bayan abkuwar lamarin, kamfanin Ethiopian Airlines ya dakatar da amfani da dukkan jiragen samansa masu samfuri iri daya da wanda ya gamu da hatsari, wato samfurin Boeing 737 MAX 8. Kuma zuwa yanzu, ba a tabbatar da lokacin sake fara amfani da jiragen ba. (Bello Wang)