in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta hukunta sama da mutane dubu 40 a shekarar 2018 saboda gurbata muhalli
2019-03-12 09:59:04 cri

Rahoton aiki da kotun kolin al'umma ta kasar Sin ta gabatar, ya nuna cewa a shekarar 2018 da ta gabata, an hukunta mutane 42,195 saboda samunsu da laifin lalata muhalli da kuma albarkatu, karuwar kaso 21 cikin 100 kan na shekarar da ta gabata ce ta.

Rahoton ya kara da cewa, kotun kolin ta kara daukar wasu matakai kan yadda za a rika hukunta manyan laifuffuka da suka shafi gurbata muhalli.

A wani labarin kuma, kotun kolin al'ummar ta bayyana cewa, kotuna dake sassan kasar, sun yanke hukunci mai tsauri kan wadanda ake zargi da aikata laifuffuka da suka shafi gurbata muhalli, inda a shekarar 2018, kotunan suka yanke hukunci kan irin wadannan laifuka har guda 2,204.

Haka kuma kotuna a sassa daban-daban na kasar Sin, sun yanke hukunci kimanin 251 kan laifukan da suka shafi muhalli da albarkatu. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China