Ma'aikatar kula da gandun daji da kare muhalli ta kasar Sin ta ce ana tuhumar jami'ai kimanin 6,219 daga larduna 10 da laifukan da suka jibinci gurbata muhalli bayan wani bincike da hukumomin kwamitin tsakiya suka gudanar tsakanin ranakun 30 ga watan Mayu zuwa 7 ga watan Yulin wannan shekara.
Sanarwar ta ce, ya zuwa yanzu, ana tsare da mutane 610, kana an aza musu tarar yuan miliyan 710 (kwatankwacin dalar Amurka miliyan 102.6), bayan kammala binciken da aka gudanar game da muhallin. (Ahmad Fagam)