in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban WHO ya ziyarci cibiyoyin kula da masu cutar Ebola a DR. Congo bayan an kai musu hare-hare
2019-03-11 09:52:41 cri

Darakta Janar na hukumar lafiya ta duniya WHO, Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya kai ziyara cibiyar kula da masu cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo, bayan wasu tsageru sun kai mata hari, ya na mai kira da a kare irin wadannan cibiyoyi yayin da ake tsaka da fuskantar barkewar cutar.

Sa'o'i kalilan bayan harin na ranar Asabar, Tedros Adhanom ya yi rangadin cibiyar birnin Butembo, wadda ita ma aka far mata a makon da ya gabata, inda ya godewa ma'aikatan cibiyar saboda jajircewarsu.

Darakta Janar din ya ce, yayin da ake ci gaba da makokin wadanda suka mutu a harin da aka kai a baya, a kokarinsu na kare hakkin lafiya, tuna jami'an lafiya da suka ji rauni da 'yan sandan da suka mutu a harin na taba masa zuciyarsa.

Ya kara da cewa, babu wani zabi, ban da ci gaba da yi wa jama'ar kasar hidima, wadanda ke cikin mutanen da suka fi rauni a duniya.

Har ila yau, jami'in ya ce WHO ta nema, kuma ta samu karin tallafi daga MDD da jami'an tsaro na yankin, domin kare cibiyoyin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China