in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta bukaci DRC da ta martaba tsarin demokuradiya
2019-01-11 10:00:42 cri
Shugaban hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Afirka Moussa Faki Mahamat, ya jaddada bukatar dake akwai ga masu ruwa da tsaki a harkokin siyasar kasar Jamhuriyar demokiradiyar Congo da su martaba tsarin Demokiradiya, tare da tabbatar da zaman lafiyar kasar.

Kalaman jami'in na AU na zuwa ne bayan da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar ta sanar da sakamakon wucin gadi na zaben shugabancin kasar.

An ruwaito Moussa cikin wata sanarwa na cewa, kamata ya yi a kalubalanci sakamakon zaben na wucin gadi bisa doron doka cikin lumana, da ma tattaunawar siyasa tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki na kasar.

Sai dai kuma Faki, ya ce yanayin da ake ciki a kasar na bukatar cimma daidaito, ta hanyar mutunta manufofin demokiradiya da 'yancin dan-Adam da ma kokarin tabbatar da zaman lafiya.

A jiya da safe ne, hukumar zaben kasar ta ayyana dan takarar adawa Felix Tshisekedi a matsayin wanda ya lashe zaben shugabancin kasar, sai dai kuma ragowar 'yan takarar sun ti watsi da sakamakon zaben. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China