in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da taro game da yanayin siyasa a jamhuriyar dimokaradiyyar Congo
2019-01-18 09:45:09 cri
A jiya Alhamis ne manyan wakilai daga kasashe mambobin kungiyar raya kudancin Afirka ta SADC, suka gudanar da taron musamman, game da lalubo hanyoyin warware takaddamar siyasa da ta kunno kai a janhuriyar dimokaradiyyar Congo, bayan kammalar zaben kasar.

Shugaban kasar Rwanda, kuma jagoran karba karba na kungiyar AU Paul Kagame ne ya jagoranci taron na birnin Addis Ababa fadar mulkin kasar Habasha. Kaza lika taron ya samu halartar firaministan Habasha Abiy Ahmed, da shugaban Afirka ta kudu Cyril Ramaphosa, da shugaba Yoweri Museveni na kasar Uganda.

Da yake tsokaci yayin bude taron, shugaba Kagame ya jinjinawa kokarin shugabannin kasashe mambobin kungiyar SADC, na zakulo hanyoyin warware sabanin da ya biyo bayan zaben Congo, yana mai nanata bukatar da ake da ita, ta hadin kan daukacin kasashen Afirka wajen shawo kan matsalolin nahiyar.

Shi kuwa shugaban hukumar zartaswar kungiyar AU Moussa Faki Mahamat, cewa ya yi da damu mataka, game da yanayin da ake ciki a janhuriyar dimokaradiyyar Congo, kuma taron na wannan karo, mataki ne na nuna goyon baya ga kasar. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China