A wata sanarwar da ma'aikatar tsaron kasar Nijer ta bayar, an ce, dakarun kungiyar Boko Haram sun kai hari ga wani sansanin soja dake jihar Diffa a daren ranar 8 ga wata, wanda ya haddasa mutuwar mutane 7 tare da raunatar mutane fiye da 20. Bangaren soja na kasar Nijer ya mayar da martani nan take, inda suka harbe dakarun kungiyar Boko Haram 38, da lalata motoci 5, sannan ta kama wani dan kungiyar, da kuma samun makamai da dama.
Sanarwar ta bayyana cewa, sojojin kasar Nijer za su dauki matakai a wannan yanki don murkushe sauran dakarun kungiyar. (Zainab)