Hukumar tsaron kasar Nijer ta gabatar da sanarwa a ranar 16 ga wata cewa, dakarun kungiyar Boko Haram sun kai hari ga wani sansanin soja na jihar Diffa dake kudu maso gabashin Jamhuriyyar Nijer a daren ranar 15 ga wata, wanda ya haddasa mutuwar mutane 8 tare da raunatar mutane 29. Bangaren soja na Jamhuriyyar Nijer ya mayar da martani tun da wuri, ya zuwa yanzu an kama dakaru 4 tare da motoci 4.
Jihar Diffa tana kan iyakar tsakanin Nijer da Nijeriya, kungiyar Boko Haram ta sha kai hare-haren ta'addanci a wannan yanki, wadanda suka haddasa mutuwa da raunatar mutane da dama. (Zainab)