in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya yi tir da harin da aka kai Somalia
2019-03-02 15:19:38 cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya yi tir da munanan hare-haren ta'addanci da aka kai Mogadishu, babban birnin Somalia.

Cikin wata sanarwa da kakakinsa Stephane Dujjaric ya fitar, Antonio Guterres ya ce ya yi imani al'ummar kasar ba za su bari irin wannan tashin hankali ya dauke hankalinsu daga kokarinsu na samun zaman lafiya da kyakkyawar makoma ba.

Ya kuma jadadda goyon bayan MDD ga al'umma da gwamnatin kasar Somalia yayin da suke kokarin cimma zaman lafiya.

A kalla mutane 30 ne suka mutu sanadiyyar wani hari da aka kai cikin wata mota a wajen wani otel dake birnin Mogadishu, ranar Alhamis da dare.

Tuni dai kungiyar Al-Shabab mai alaka da Al-Qaeda ta dauki alhakin kai harin, tana mai cewa otel din ta kai wa hari, wanda ya yi fice tsakanin 'yan siyasa da jami'an gwamnati da kuma manyan 'yan kasuwa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China