in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi Allah wadai da harin da aka kaddamar kan dakarun wanzar da zaman lafiya a Mali
2019-02-24 16:02:55 cri
Kwamitin sulhun MDD (UNSC) ya yi Allah wadai da harin da aka kaddamar kan dakarun wanzar da zaman lafiya na MDD na gamayyar kasashen duniya dake aiki a Mali wato (MINUSMA) a yankin Siby.

"Mambonin kwamitin sulhun MDD sun bayyana rashin jin dadinsu da kuma sakon jajantawa da ta'aziyya ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su, da kuma mutanen Guinea da tawagar ta MINUSMA," in ji sanarwar UNSC.

Kwamitin sulhun MDD ya yi Allah wadai da duk wani yunkuri da ya shafi tsarawa, aiwatarwa da kuma daukar nauyi dukkan hare-hare kan dakarun wanzar da zaman lafiyar na MINUSMA duba da irin namijin kokarin da suke yi na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a karkashin yarjejeniyar kwamitin sulhun MDD. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China