in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD yana maraba da yarjejeniayr zaman lafiyar CAR
2019-02-14 11:01:53 cri
A jiya Laraba kwamitin sulhun MDD ya yi maraba da yarjejeniyar zaman lafiyar da aka sanya hannu kanta tsakanin gwamnatin jamhuriyar tsakiyar Afrika (CAR) da kuma kungiyoyin masu dauke da makamai su 14.

Mambobin kwamitin sulhun MDDr sun bayyana sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiyar ta ranar 6 ga watan Fabrairu a babban birnin kasar Bangui da cewa, wani muhimmin mataki ne wajen samun dauwamammen zaman lafiya da kwanciyar hankali a CAR da kuma samun cikakken tsarin shugabanci a kasar, in ji sanarwar.

Mambobin MDDr sun bukaci dukkan masu ruwa da tsaki a CAR da su aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiyar da kyakkyawar zuciya kuma ba tare da jinkiri ba. Kana mambobin sun bayyana muhimmancin aiwatar da yarjejeniyar bisa adalci da kuma ba da cikakkiyar dama ga kungiyoyin fararen hula, da mata da matasa cikin shirin zaman lafiyar.

Haka zalika kwamitin MDDr, ya bukaci dukkan kungiyoyin masu dauke da makamai da su kawo karshen dukkan tashe-tashen hankula da gallazawa fararen hula, da jami'an kiyaye zaman lafiya, da masu bayar da tallafin jin kai, kuma su guji wargaza hanyoyin zaman lafiya, kana su baiwa jami'an bayar da agajin jin kan al'umma damar shiga wuraren bayar da tallafin da kuma bai jama'a 'yancin walwala. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China