Za a nuna taron manema labaru game da zaman taro na biyu na CPPCC karo na 13 kai tsaye
Gobe Asabar 2 ga watan Maris da karfe 3 da yamma agogon Beijing, za a shirya taron manema labaru game da zaman taro na biyu na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta jama'ar kasar Sin wato CPPCC a ofishin watsa labaru na zauren babban dakin taron jama'a na Beijing, inda kakakin taron zai amsa tambayoyin manema labaru na cikin gida da na waje game da yanayin babban taron.
Gidan rediyon kasar Sin na rukunin CMG zai watsa abubuwan dake gudana a taron ta shafin CRI online na Turanci, da manhajan China Plus kai tsaye,
A lokaci guda kuma, za a nuna hoton bidiyo game da taron kai tsaye ta anyar shafin Sinanci na CRI Online. (Bilkisu)