Sin: Ya kamata a mutunta 'yancin kasar Venezuela
Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ya amsa wata tambayar da manema labaru suka yi masa dangane da batun Venezuela, a yau Litinin a birnin Beijing na kasar Sin, inda ya furta cewa, kasar Sin na fatan ganin an tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar ta Venezuela, kuma sam ba ta yarda da yadda aka tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar ba. Don haka kasar Sin ta bukaci gamayyar kasa da kasa su mutunta 'yanci da ikon mulkin kai na kasar Venezuela, sa'an nan su taimakawa kasar ta yadda za ta daidaita yanayin da ake ciki a kasar. (Bello Wang)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku