in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana maraba da shugabannin kamfanonin kasashen waje da su kawo ziyara da yin ciniki a kasar Sin
2019-02-22 20:10:19 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau Juma'a 22 ga wata cewa, za a tabbatar da tsaron duk wani dan kasar waje muddin yana martaba dokokin kasar Sin. Gwamnatin kasar Sin za ta ci gaba da samar da yanayin ciniki mai kyau ga kamfanonin kasashen waje, kana tana yin maraba da shugabannin kamfanonin kasashen waje da su kawo ziyara da yin ciniki a kasar Sin.

Geng Shuang ya yi nuni da cewa, bisa kididdigar da hukumomin Sin da abin ya shafa suka fitar, ta nuna cewa, yawan sabbin kamfanoni masu jarin waje a kasar Sin a shekarar 2018 ya kai fiye da dubu 60, wanda ya karu da kashi 69.8 cikin dari bisa na shekarar 2017. Yawan jarin waje da aka yi amfani da shi a shekarar ya kai dala biliyan 135, wanda ya karu da kashi 3 cikin dari. An samu wadannan karuwa ne sakamakon zirga-zirgar mutane a tsakanin Sin da kasashen waje, ciki har da 'yan kasuwa na kasashen waje da dama da suka kawo ziyara da ma yin shawarwarin ciniki a kasar Sin. Idan kasar Sin ba ta tabbatar da tsaro ba, ba za a samu irin wannan Alkalamu ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China