Xi Jinping ya aika da sakon taya murnar bude bikin shekarar musaya tsakanin kafofin watsa labaru na Sin da ASEAN
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aika da sakon taya murnar bude bikin shekarar musaya tsakanin kafofin watsa labaru na Sin da ASEAN da aka shirya a jiya Laraba.
A cikin sakon, Xi ya nuna cewa, dangantakar dake tsakanin Sin da ASEAN na shiga wani sabon zamani na ci gaba a dukkan fannoni. Yana fatan kafofin watsa labaru za su inganta sada zumunci da hakikanin hadin kai a tsakanin bangarorin biyu. (Bilkisu)