in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babbar hukumar yaki da rashawar kasar Sin ta bayyana bangarorin da zata bada fifiko a 2019
2019-02-21 09:38:15 cri
Hukumar dake yaki da rashawa ta kasar Sin ta ayyana muhimman bangarorin da za ta fi mayar da hankali a ayyukanta na shekarar 2019, wanda ya kunshi cigaba da gina manufofin jam'iyya a matsayin wani babban jigo da kuma tabbatar da da'a, da sanya ido kan harkokin tafiyar da sha'anin ayyukan gwamnatin kasar.

Wani rahoto ne ya bayyana hakan a jiya Laraba, wanda aka gabatar a taron kwamitin da'a na kawamitin tsakiya karo na 19 (CCDI) na jam'iyyar Kwaminis (CPC), wanda babban jami'in kwamitin Zhao Leji ya gabatar a ranar 11 ga watan Janairu.

Tabbatar da gina manufofin jam'iyya zai kasance muhimmin ginshiki, wanda ta haka ne za'a samu nasarar kakkabe dukkan wasu ayyukan da ba su dace ba, inji rahoto.

Tsare tsare da kuma irin matakan da ake bi wajen sanya ido za'a aiwatar da su ne domin inganta sha'anin ayyukan gwamnati baki daya, inji rahoton.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China