in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana fatan Iran za ta kara taka rawa a harkokin shiyya-shiyya
2019-02-19 20:27:12 cri

Mamba a majalisar gudanarwar kasar Sin kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya ce kasarsa na martaba rawar da Iran ke takawa a harkokin shiryya-shiyya, tana kuma fatan za ta kara taka muhimmiyar rawa a wannan fanni.

Wang ya bayyana hakan ne a yau Talata, yayin ganawarsa da takwaransa na kasar Iran Mohammed Javad Zarif a nan birnin Beijing. Ya ce kasashen Sin da Iran kasashe ne masu tarihin dubban shekarun na wayewar kai da al'adun kana duk da canje-canjen dake faruwa a duniya, kasashen biyu, za su ci gaba da karfafa alakarsu bisa manyan tsare-tsare da kiyaye tare da karfafa alakarsu ta dogon lokaci, a kokarin bullo da sabbin abubuwa cikin hadin gwiwar dake tsakaninsu.

A nasa jawabin Zarif, ya ce, bangaren Iran yana martaba alakar dake tsakaninsa da kasar Sin, kana yana daukar kasar Sin a matsayin muhimmiya kuma aminiyar hadin gwiwa a dukkan fannoni.

Ya kuma bayyana kudurin kasarsa na shiga a dama da ita wajen gina shawarar ziri daya da hanya daya, yana mai cewa, shawarar tana da muhimmanci na musamman ga kasashen na Sin da Iran.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China