in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sama da mutane 60 ake fargabar sun mutu yayin da suke hakar zinare, biyo bayan aukuwar ambaliyar ruwa a Zimbabwe
2019-02-16 15:46:02 cri
Sama da mutane 60 ne aka yi ammana sun mutu, a wani wurin hakar ma'adinai, bayan wata madatsar ruwa dake kusa da wurin ta yi ambaliya, a lardin yammacin Mashonaland na kasar Zimbabwe.

Ministan kula da kananan hukumomi da aikin gwamnati da tsarin samar da gidaje na kasar, July Moyo, ya ce adadin masu hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba da al'amarin ya rutsa da su ka iya kai wa 60 zuwa 70.

Cikin wata sanarwa da ya fitar jiya Juma'a, July Moyo ya ce babu kwakkwarar fatan samu wadanda suka tsira, biyo bayan mamakon ruwa da aka yi a yankin da daren ranar.

Masu aikin ceto sun yi nasarar fitar da ruwa daga cikin ramukan, inda za a fara aikin zakulo gawarwaki a yau Asabar.

Shugaban Zimbabwe Emmerson Mnangagwa ya ayyana lamarin a matsayin annobar da ta aukawa kasar.

Ministar kula da harkokin lardin yammacin Mashonaland Mary Mliswa-Chikoka, ta ce lamarin zai zama izina ga hukumomin kula da hakar ma'adinai da masu aikin hakar, kan bukatar rugumar hanyoyin kariya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China