in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Zimbabwe ya nanata aniyarsa na tattaunawa da 'yan adawa
2019-02-08 16:08:33 cri
Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa ya bayyana a jiya Alhamis cewa a shirye yake ya shirya babban taron kasa don tattaunawa da jam'iyyun hamayya don tabbatar da ci gaban kasar.

"Kofa a bude take a kokarin da muke na neman yadda za mu samarwa kasarmu kyakkyawar makoma, da ci gaba, da ingantacciyar rayuwa ga al'ummarmu," Mnangagwa ya bayyana hakan ne cikin wani jawabi wanda aka karanta a madadinsa a taron addu'o'i na kasa na mabiya addinin kirista.

A ranar Laraba Mnangagwa, ya gana da 'yan takarar neman shugabancin kasar su 20 wadanda suka tsaya takarar a zaben da aka gudanar a bara domin tattaunawar bayan zabe da nufin lalibo bakin zaren warware manyan kalubalolin dake addabar kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China