Shugaban ya yi wannan furucin ne, a wajen wani bikin kamfen da aka yi a Ado-Ekiti dake kudancin kasar Najeriya, inda ya ce gwamnatinsa, na ta kokarin dakile cin hanci da rashawa, sai dai aikin na cikin wani hali mai wuya. Duk da haka, shugaba Buhari ya yi kira ga wadanda za su jefa kuri'a a yayin zaben, da su nuna masa goyon baya.
Ya ce yana da cikakken imani kan cika alkawarin da ya dauka a shekarar 2015, wato kau da cin hanci da rashawa tun daga tushensa. (Bello Wang)