in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Najeriya na sanya ido kan masu adawa
2019-02-05 16:21:01 cri
Ministan watsa labarai a tarayyar Najeriya Lai Mohammed, ya ce gwamnatin kasar za ta zuba ido matuka kan yanayin da kasar ke ciki ta fuskar tsaro, domin kaucewa tashin hankali. Kaza lika gwamnatin na gargadin 'yan adawa da kaucewa daukar matakan ta da husuma a lokacin, ko bayan babban zaben kasar dake tafe nan da 'yan kwanaki masu zuwa.

Lai Mohammed wanda ke wannan tsokaci yayin wani taron manema labarai a Abuja, fadar mulkin kasar a jiya Litinin, ya ce wasu daga bangaren 'yan adawa a kasar na daukar zaben a matsayin ko a mutu ko ai rai wanda hakan bai dace ba.

Jami'in ya kara da cewa, wasu bayanan sirri sun tabbatar da cewa, akwai wani bangare na 'yan adawar dake son daukar matakan gurgunta zaben dake tafe, ciki hadda shirin wasu, na aikewa da tawagogin mutane goma-goma zuwa wasu manyan kasashen duniya, da nufin yada karairayi game da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari.

Za dai a gudanar da zaben shugaban kasa da 'yan majalisun dokokin tarayyar Najeriya ne a ranar 16 ga watan nan na Fabarairu, kana a gudanar da na gwamnoni da 'yan majalisun jihohi a ranar 2 ga watan Maris. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China