in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO: A bara mutanen da suka rasu sakamakon cutuka masu nasaba da daji a Najeriya sun kai 41,000
2019-02-05 16:24:35 cri
Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta ce a shekarar 2018 da ta gabata, adadin mutane da suka rasu sakamakon cutuka masu nasaba da cutar daji ko Cancer a tarayyar Najeriya sun kai 41,000, cikin jimillar mutane 166,000 da cutar ta shafa a fadin kasar.

Jagoran tawagar ayyukan gaggawa, na WHO a Najeriyar Clement Peter ne ya bayyana hakan a jiya Litinin, yayin taron karawa juna sani da aka gudanar albarkacin ranar cutar Cancer ta kasa da kasa ta bana, wadda ke gudana duk shekara a ranar 4 ga watan Fabarairu.

Taken bikin na bana dai shi ne "Ni ne kuma zai yi nasara."

A Najeriya da ma wasu kasashen Afirka da dama, masana sun fi alakanta dalilan kamuwa da cutar da shan taba, da giya, da rashin motsa jiki, da gurbatar yanayi, da kuma cin abinci maras dacewa da gina jiki. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China