in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Sin da Sudan sun aike wa juna sakon taya murna
2019-02-04 14:44:58 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, da takwaransa na kasar Sudan Omar Al-Bashir, sun aike wa juna sakwanni a yau Litinin, don taya juna murnar cika shekaru 60 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasashensu.

Cikin sakonsa, shugaba Xi Jinping na kasar Sin, ya bayyana fatansa na ganin kasashen Sin da Sudan su karfafa hadin gwiwa, musamman ma bisa tsarin shawarar "Ziri Daya da Hanya Daya", da kokarin aiwatar da sakamakon da aka samu a taron dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da ya gudana a birnin Beijing a bara.

Shi kuwa a nasa bangaren, shugaba Al-Bashir na kasar Sudan cewa ya yi, kasarsa na son kara yaukaka zumuncin dake tsakaninta da kasar Sin, da amsa kiran da Sin ta yi, na neman tabbatar da makoma mai kyau ta bai daya ga daukacin bil Adama dake duniyarmu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China