in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya aike da sakon ta'aziyya ga takwaransa na kasar Philippines
2019-01-29 20:26:26 cri
A yau Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da sakon ta'aziyya ga takwaransa na kasar Philippines, Rodrigo Duterte, bisa harin bom da aka kaiwa lardin Sulun dake kasar a kwanan baya.

Cikin sakonsa, shugaba Xi ya jaddada cewa, kasar Sin tana kin jinin duk wani irin aiki na ta'addanci, kuma tana Allah wadai da hare-haren da aka kai wa fararen hula, wadanda ba su san hawa ba, ba su san sauka ba. Ya ce kasar Sin tana da burin aiki tare da Philippines, gami da sauran kasashe daban daban, don yaki da ta'addanci, da tabbatar da kwanciyar hankali a duniyarmu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China