in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sinawa mazauna kasashen waje na da yakini game da makomar kasarsu
2019-02-04 13:34:24 cri
Jawabin shugaban kasar Sin Xi Jinping na taron bikin sabuwar shekarar gargajiya ta kasar da aka yi jiya Lahadi a birnin Beijing, ya ja hankalin Sinawa mazauna kasashen waje, la'akari da yadda ya bayyana irin nasarorin da kasar ta samu a shekarar da ta gabata, da kuma sa ran samun kyakkyawar makoma.

Ren Limin, shugaban kungiyar Sinawa mazauna Faransa, ya ce yana alfahari da ci gaba cikin sauri da kasar Sin ta samu karkashin jagorancin JKS.

Ya ce kasar ta samu gagarumin nasarori wajen aiwatar da gyare-gyare cikin gomman shekarun da suka gabata, inda ta kara arziki da karfi.

Shi kuwa Liu Kai, mataimakin shugaban kungiyar yayata hadin kan Sinawa a Birtaniya, ya ce ba sakon gaisuwa kadai jawabin shugaba Xi ya kai ga Sinawa mazauna Birtaniya ba, domin ya kara karfafa yakininsu na samun kyakkyawar makoma.

Liu wanda kuma shi ne shugaban gidauniyar YanFu, yakinin nasu ya samo asali ne daga tabbacin da suke da shi cewa, muddin jama'a suka dogara da juna, to babu kalubalen da ba za su iya shawo kansa ba, kana babu wani buri da ba za su cimma ba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China