Geng Shuang ya kara da cewa, kasar Amurka tana ta kokarin shafa wa wasu kamfanonin kasar Sin kashin kaza, da niyyar gurgunta harkokinsu a kasashe daban daban. Hakan, a cewar jami'in na kasar Sin, wata makarkashiyar da aka kulla ce tare da wani buri na siyasa. Saboda haka, kasar Sin ta bukaci Amurka da ta daina cin zarafin kamfanonin kasar Sin, gami da nuna adalci gare su. Sa'an nan a nata bangare, kasar Sin za ta yi iya kokarin kare hakkin kamfanoninta. (Bello Wang)