in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD za ta tallafawa matan dake fafutukar gina zaman lafiya a Libya
2019-01-24 10:50:45 cri
Maria do Valle Ribeiro, mataimakiyar wakiliyar musamman ta MDD a kasar Libya, ta nanata aniyar tallafawa kokarin da mata ke yi a fafutukar wanzar da zaman lafiya da bunaksa cigaban al'umma.

Jami'ar ta MDD ta bayyana hakan ne a lokacin ganawa da Laila Al-Lafi, babbar jami'ar sashen kula da shirin raya cigaban mata da tallafa musu na gwamnatin Libya.

"Rawar da matan Libya ke takawa wajen gina zaman lafiya da raya cigaba yana da girman gaske," Valle Ribeiro ce ta bayyana hakan.

An kafa cibiyar tallafawa mata karkashin doka mai lamba ta 11 wanda aka amince da ita karkashin yarjejeniyar MDD a kasar Libya, wanda bangarorin 'yan adawa a Libyan suka rattaba hannu kan yarjejeniyar a karshen shekarar 2015, da nufin kawo karshen dambarwar siyasar kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China