in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun Najeriya sun kashe barayin shanu 58 a shiyyar arewacin kasar
2019-01-24 10:07:01 cri
Dakarun tsaron Najeriya sun hallaka barayin shanu 58 da kuma ceto mutane 75 wadanda aka yi garkuwa da su a yayin da dakarun tsaro ke cigaba da aikin farautar barayin shanun da masu yin garkuwa da mutane a jahar Zamfara dake arewacin Najeriya.

A wata sanarwa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya samu a jiya Laraba, kakakin rundunar wanzar da tsaro ta musamman ta Operation Sharan Daji, Clement Abiade, ya ce dakarun sun yi arba da babbar tawagar mayakan 'yan bindigar dake dauke manyan makamai na zamani a dazukan Dumburum da Gando ranar Lahadi.

A 'yan shekarun baya bayan nan jahar Zamfara, tana fuskantar kalubalolin tsaro musamman a yankunan karkarar jahar, wanda a baya ake samun kwanciyar hankali amma a yanzu ake fuskantar rikici tsakanin makiyaya da manoma.

Hare haren da 'yan bindigar suka kaddamar a jahar Zamfara ya yi sanadiyyar hallaka rayukan gomman mutane kana wasu dubbai suka tsere daga gidajensu tun a watan Disambar shekarar 2018.

A watan Disambar gwamnatin Najeriya ta tura karin jami'an tsaro, da jirgin saman yaki na sojoji zuwa jahar ta Zamfara da jahar Sokoto mai makwabtaka domin fatattakan mayakan masu dauke da makamai. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China