in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane na kara barin muhallansu a yankin arewa maso gabashin Najeriya
2019-01-23 09:12:46 cri
Wani rahoto da ma'aikatan kungiyoyin ba da agaji suka fitar ya nuna cewa, daga watan Nuwanba zuwa wannan lokaci, kimanin mutane 80,000 ne suka gujewa matsugunansu a yankin arewa maso gabashin Najeriya, sakamakon arangawa tsakanin kungiyoyi masu dauke da makamai da dakarun sojan kasar.

Mataimakin kakakin babban sakataren MDD Farhan Haq ne ya bayyana hakan yayin taron majalisar da aka saba gudanarwa, yana mai cewa wannan adadi ya hada da mutane miliyan 1.8 da tuni suka gujewa matsugunan nasu a yankin arewa maso gabashin kasar.

Jami'in ya ce, su ma kungiyoyin kasa da kasa da hukumomin bayar da agaji sun nuna damuwarsu game da illar da karuwar tashin hankali da matsalar tsaro ka iya haifarwa, a daidai gabar da ake shirin gudanar da zaben shugabancin kasar a ranar 16 ga watan Fabrairun dake tafe, ciki har da karuwar zirga-zirgar jama'a da karancin ayyukan jin kai a wasu yankunan.

A don haka MDD ke kira ga dukkan bangarorin da rikicin ya shafa, da su kare fararen hula da dukiyoyinsu kana su mutunta dokokin kasa da kasa. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China