in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamaru da Najeriya za su hada gwiwa wajen yaki da rashawa
2019-01-17 10:23:56 cri
Kasashen Najeriya da Kamaru sun fara lalibo hanyoyin hadin gwiwa da nufin yaki da rashawa a kasashen biyu, jami'an hukumar yaki da rashawa na Kamaru ne suka tabbatar da hakan a jiya Laraba.

Jami'an hukumar yaki da rashawa na Kamaru (CONAC) da na hukumar yaki da rashawa ta Najeriya (EFCC), sun gana a Yaounde a jiya Laraba domin tsara wasu ka'idojin yin hadin gwiwa tare.

"Mun zo wannan waje ne da nufin samun fahimtar juna game da danganta, da musayar shawarwari a tsakaninmu," Mohammed Abba Umar, daraktan gudanarwar hukumar EFCC, shi ne ya bayyana hakan ga 'yan jaridu.

"Rashawa ba matsala ce ta kasa daya tilo ba, sai dai matsala ce da ta shafi dukkan kasashen Afrika baki daya, kuma mun yaba da irin hadin gwiwa dake tsakanin Kamaru da Najeriya," in ji shugaban hukumar ta CONAC, Dieudonne Massi Gams.

Badakalar kudaden haram tsakanin kan iyakokin Kamaru da Najeriya na ci gaba da karuwa kuma akwai bukatar a gaggauta daukar matakan dakile su tare da cafke wadanda ke da hannu, in ji jami'an. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China