in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kotun duniya: Laurent Gbagbo ba shi da laifi
2019-01-16 10:41:06 cri
Alkalan kotun duniya mai shari'ar masu aikata manyan laifuka sun sanar a jiya Talata cewa, tsohon shugaban kasar Kodibwa, Laurent Gbagbo, bai aikata laifin keta hakkokin bil Adama ba, don haka ya kamata a sake shi nan take.

Wannan sanarwa ta ce, yawancin alkalan kotun duniya sun yarda da cewa, masu gabatar da kara ba su samar da cikakkun shaidu, na tabbatar da laifukan da ake zargin Laurent Gbagbo da aikatawa ba, ciki hadda haddasa tashin hankalin da ya abku a kasarsa bayan babban zaben da ya gudana a shekarar 2010.

Bayan kammala babban zaben kasar Kodibwa a karshen shekarar 2010, shugaban kasar na lokacin Laurent Gbagbo, da mai jagorantar 'yan adawa Alassane Ouattara, dukkansu sun ayyana kan su a matsayin masu nasara a zaben, kuma sun yi rantsuwar kama aiki bisa radin kansu. Daga bisani, masu goyon bayan mutanen 2 sun yi taho-mu-gama har tsawon watanni 5, lamarin da ya haddasa rasa rayukan mutane kimanin 3000, kana wasu fiye da miliyan 1 suka galabaita.

A ranar 11 ga watan Afrilun shekarar 2011, aka kama Laurent Gbagbo a Kodibwa, sakamakon yadda masu gabatar da kara na kotun duniya, suka zarge shi, da masu goya masa baya, da daukar matakan karfin tuwo kan jama'a masu goyon bayan Alassane Ouattara, zargin da Laurent Gbagbo ya karyata. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China