in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in Sudan sun sha alawshin maido da zaman lafiya yayin da ake fama da bore a fadin kasar
2019-01-03 09:48:28 cri
A jiya Laraba ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar Sudan ta jaddada aniyarta na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duk fadin kasar, kamfanin dillancin labaran kasar SUNA shi ne ya ba da wannan rahoto.

An jiyo ministan harkokin cikin gidan kasar Sudan Musa Mohamed Ali Madibo, yana cewa "Dokar kasar ta ba da damar a shirya zanga zangar lumana amma idan an samu amincewar hukumomin kasar, amma kada zanga zangar ta haifa da yin fito na fito, ko tashin hankali, ko kuma rashin zaman lafiya a kasar".

Ministan ya bukaci 'yan kasar da su taimaka wajen dakatar da duk masu yunkurin wargaza zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar.

Madibo ya ce, an kafa wasu kwamitoci na musamman tun bayan barkewar zanga zanga a duk fadin kasar, an bayyana cewa kwamitocin da aka kafa sun riga sun fara aikin tantance adadin mutanen da suka hallaka, da kuma irin hasarar da aka tafka na dukiyar gwamnati da bangarori masu zaman kansu.

Tun a ranar 19 ga watan Disamba ne, yankuna da dama a kasar Sudan, ciki har da babban birnin kasar Khartoum, suke cigaba da fuskanta mummunar zanga zanga sakamakon tabarbarewar tattalin arzikin kasar da tashin farashin kayayyakin masarufi a kasar.

A bisa alkaluman da gwamnati ta fitar, mutane 19 ne aka hallaka a lokacin zanga zangar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China