in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sudan ya yi alkawarin gyare-gyare a tattalin arzikin kasar
2018-12-25 10:23:07 cri
Shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir a jiya Litinin ya sanar da alkawarinsa na daukar matakan gyare-gyare a fannin tattalin arzikin kasar don neman kyautata zaman rayuwar jama'ar kasar.

Kamfanin dillancin labarai na kasar SUNA ya ruwaito cewa, shugaba AL-Bashir ya yi furucin ne yayin wata ganawar da ya yi da kwamandan hukumar leken asiri da aikin tsaro na kasar, wanda ya kasance karo na farko da ya furta hakan, tun bayan da aka samu barkewar zanga-zanga a kasar don nuna damuwa kan lalacewar tattalin arzikin kasar.

Ban da haka, shugaban ya yi kira ga jama'ar kasar Sudan da kar su saurari jita-jita da magance daukar matakai na takaddama da gwamnati. Ya ce zai dauki takamaiman matakai don kwantar da hankalin jama'a da ba su tabbaci kan tsarin hada-hadar kudi na kasar. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China