in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da dokar ta baci a birnin Atbara na kasar Sudan
2018-12-20 14:00:56 cri
Mahukunta a jihar Nahr Al-Neel ta kasar Sudan, sun ayyana dokar ta baci a birnin Atbara, birnin mafi girma a jihar, tare da sanya dokar hana zirga zirgar jama'a, bayan barkewar wani bore.

A cewar kafar yanar gizo ta Ashorooq, an ayyana wadannan matakai ne bayan kammala zaman kwamitin tsaro na jihar. Ibrahim Mukhtar, shi ne kakakin gwamnatin jihar, ya kuma tabbatar da daukar wannan mataki na gwamnati.

A wani ci gaban kuma, jam'iyyar NCP mai mulkin kasar ta yi tir da barkewar tarzoma a birnin na Atbara. A cewar kakakin jam'iyyar Ibrahim Al-Siddiq, duk wani dan kasa na da ikon bayyana albarkacin bakin sa ta hanyar da ta dace, amma abun da ya wakana a Atbara, sam bai dace da yanayi na wanzar da zaman lafiya da lumana ba.

Ya ce zanga zangar Atbara wani yunkuri ne na wargaza tsaro da zaman lafiya, kuma gwamnati ba za ta lamunci duk wani mataki na gurgunta zaman lafiya ba.

Yayin zanga zangar dai an kona helkwatar jam'iyyar mai mulki dake Atbara, da babban ofishin kananan hukumomi, da wani gidan mai.

Rahotanni sun nuna cewa, da fari an fara zanga zangar ne cikin lumana, kafin daga bisani ta rikide zuwa tashin hankali da ya sabbaba barnata kayayyaki. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China