in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in AU ya yi Allah wadai da harin da aka kaddamar a sansanin AMISOM dake Somalia
2019-01-03 09:09:29 cri
Babban wakilin kungiyar tarayyar Afrika a Somalia ya yi Allah wadai da harin da aka kaddamar kan sansanin dakarun kiyaye zaman lafiyar kungiyar tarayyar Afrika dake Somalia (AMISOM) a birnin Mogadishu a ranar Talata.

Francisco Madeira, wakilin musamman na kungiyar AU a Somalia, ya ce harin wanda mayakan al-Shabab suka kaddamar, wanda bai samu nasarar kaiwa inda suka so ba, hakan alamu ne dake nuna cewa mayakan ba su nuna tausayi ga rayuwar bil adama.

Abubuwan fashewa 7 ne mayakann suka harba sansanin na AMISOM a ranar Talatar, sai dai dukkaninsu ba su yi nasarar kaiwa inda suka so su kai ba.

Wasu ma'aikatan MDD 2 da wani dan kwangila guda sun samu raunuka a lokacin kai harin na sari ka noke a ranar Talata bayan da mayakan suka harba abubuwan fashewar 7 a harabar ginin MDD.

Kungiyar 'yan ta'adda ta al-Shabab sun dauki alhakin kaddamar da harin. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China