in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Nijer da Faransa sun dauki matakan soja na hadin gwiwa don yaki da ta'addanci
2018-12-30 16:53:15 cri
Ma'aikatar harkokin tsaron jamhuriyar Nijer ta bayyana a ranar 29 ga wata cewa, sojojin Nijer da na kasar Faransa sun dauki matakan soji na hadin gwiwa a jihar Tillabéri dake yammacin jamhuriyar Nijer a daren ranar 27 zuwa wayewar gari na ranar 28 ga wata, inda aka hallaka 'yan ta'adda 15.

Ministan tsaron jamhuriyar Nijer Kalla Moutari ya bayyana a wata sanarwar cewa, wannan ne muhimmiyar nasarar da sojojin kasashen biyu suka samu a wannan yanki, kasar Nijer za ta ci gaba da yaki da ayyukan ta'addanci da muggan laifuffuka.

Bisa labaran da kafofin watsa labaru na kasar Nijer suka bayar, baya ga harbe 'yan ta'adda 15, sojojin kasashen biyu sun lalata motoci 21 tare da samun wasu makamai. Kuma babu wani soja daga kasashen biyu da ya mutu ko jin rauni a yayin artabun da suka yi da mayakan 'yan ta'addan.

Jihar Tillabéri tana yammacin kasar Nijer. A shekarun baya baya nan, ana samun yawan hare-haren kungiyar 'yan ta'adda a yankunan dake tsakanin yammacin kasar Nijer da kasar Mali da kasar Burkina Faso, wadanda suka haddasa mutuwa da raunata mutane da dama. A ranar 1 ga watan Disamba, an kai hari kan wani gidan 'yan sanda dake jihar, wanda ya haddasa mutuwar mutum guda. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China