Cikin wata sanarwa da ya fitar, Kakakin hukumar Tony Orilade, ya ce sun samu kiran waya da dama da sakonnin e-mail dake neman tabbacin ko sun tsare 'ya'yan Atiku Abubakar kamar yadda ake zargi, inda ma wasu ke cewa sun kai samame gidan ne domin neman takardun kudaden ketare.
Sai dai Ministan yada labarai na kasar Lai Mohammed, ya ce bangaren adawar na shirya labarai na bogi game da gwamnatin shugaban Kasar Muhammadu Buhari gabanin zaben 2019.
Ministan ya ce tun daga shekarar 2017, gwamnatin ke bayyana damuwa game da yada labaran bogi. (Fa'iza Mustapha)